Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {A.S} - ABNA : Tashar talabijin ta Rusiyal Yawm ta nakalto Basil yana fadar haka a shafinsa na twitter a jiya Litinin. Ya kuma kara da cewa maido da kudaden kasar wadanda manya-manyan yan siyasa, yan majalisar dokoki da kuma wadanda suke fada a ji a kasar shi ne babban abinda yakamata a sanya a gaba don kubutar da tattalin arzikin kasar daga rushewa kwatakwata.
Shugaban jam’iyyar ‘Jam'iyyar Yancin Mutanen Kasa’ ya kara da cewa jita jita ta cewa Iran ta mamaye al-amura a kasar Lebanon kariya ce, kuma wata dabara ce ta kwace ikon kasar wanda wasu 'yan siyasa masu fada a ji a kasar suke yadawa don cimma mummunan manufofinsu.
Basil ya kammala da cewa, a irin wannan halin dole ne mutanen kasar su damu, su kuma nuna rashin amincewarsu da yadda al-amura suke tafiya a kasar.
342/